Sports
Ahmed Musa Zai Gwangwajen Tawagar Flamingos Da Kyautar N3m
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kyaftin din Super Eagles, Ahmed Musa ya yi alkawarin Naira miliyan uku ga tawagar kwallon kafar mata ta Najeriya ’yan kasa da shekara 17.
Kyaftin din zai gangwaje tawagar wacce ake yi wa lakabi da Flamingos a sakamakon samun nasarar lashe kyautar tagulla a Gasar Kofin Duniya ta mata ‘yan kasa da shekara 17 ta bana.
Matsalar abinci na iya ta’azzara a Najeriya yayin da Rasha ta fice daga yarjejeniyar fitar da hatsi
Tawagar ta Flamingos dai ita ce ta doke tawagar Jamus da ci uku da biyu yayin fafatawar neman mataki na uku da suka yi ranar Lahadi a Mumbai, babban birnin Kasar Indiya.
Flamingos ta doke tawagar ta Jamus a bugun daga kai sai mai tsaron raga bayan sun tashi kunnen doki 3-3.
Daily Trust ta rawaito cewa Cikin wani sakon taya murna da ya wallafa a shafinsa na Twitter, Ahmed Musa ya ce, “Miliyan uku lakadan na jiranku a Abuja.”
Wannan nasara da Najeriya ta samu, ya sa yanzu ta zamo ta biyu a Nahiyar Afirka da su ka kai ga wannan nasarar bayan kasar Ghana wacce ita ma ta ci lambar tagulla a irin wannan gasar a 2012.
Tawagar matan Sfaniya ce dai ta lashe Gasar Kofin Duniyar ta mata ’yan kasa da shekara 17 yayin da ta lallasa tawagar Columbia da ci daya mai ban haushi a ranar Lahadi.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
