Business
Taron Zuba Jari na Afirka ya sanar da zuba jarin dala biliyan 31 a Afirka
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Taron Zuba Jari na Afirka na 2022 ya sanar da zuba jarin dala biliyan 31 a Afirka da zimmar farfado da tattalin arziki da kuma ababen more rayuwa a nahiyar.
Taron na kwana uku wanda bankin ci gaban Afirka da masu hulda da shi suka shirya, ya tattaro manyan jagororin gwamnati da hukumomi masu zaman kansu wadanda ke son zuba jari a Afirka.
COP 27: Ambaliyar Ruwa A Najeriya, Da Wasu Ya Zama Wani Bangare Na Abun Tattaunaw
Shugabannin Liberia da Ghana da Tanzania da Habasha da Zimbabwe da kuma Ivory Coast dukkansu sun nuna bkatar jano hankalin masu zuba jari zuwa nahiyar.
Hakan kuma na zuwa ne a daidai lokacin da yawancin ƙasashen Afirka ke kokarin farfadowa daga bugun da korona ta yi musu da kuma wahalhalu da biyo bayan mamayar Ukraine da Rasha ta yi, inda suka ce taron wata dama ce garesu na jawo hankalin masu zuba jari.
Taron Zuba Jarin na Afirka a taruka uku da suka gabata, sun samu nasarar zuba jari d aya kai dala biliyan 110 zuwa Afirka.
