News
An kama mutum 600 a Chadi saboda ‘shiga zanga-zanga’
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumomi a Chadi sun ce an kama sama da mutum ɗari shida har da ƙananan yara tare da tasa ƙeyarsu zuwa gidan yari sakamakon zanga-zangar baya-bayan nan da aka yi.
Mai gabatar da ƙara ya ce akasarin mutanen sun bayyana gaban kotu.
2023: Kotu Ta Hana ‘Yan Takarar Majalisar APC 16 Yin Takara A Ribas
Ƙungiyoyin ƴan adawa sun kira gangamin domin tunawa da ranar da sojoji tun farko suka yi alƙawarin miƙa mulki kafin tsawaita wa’adinsu.
Kimanin mutum hamsin ne suka mutu, lamarin da ya janyo suka daga ƙasashen duniya.
Hukumomi sun ce sojoji da dama sun mutu. Shugaban Chadi, Janar Mahamat Idriss Derby ya zargi masu zanga-zangar da ƙoƙarin iza yaƙin basasa.
Advertisements
