Connect with us

News

Sojoji sun kashe ƙasurgumin ɗan fashi a Kaduna

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Sojojin Najeriya sun ce sun kashe wani jagoran ƴan fashin daji a jihar Kaduna, mai suna Dogo Maikasuwa.

 

Advertisement

Wata sanarwa da kwamishinan harkokin cikin gida da tsaro na jihar, Samuel Aruwan ya fitar, ranar Juma’a, ta ce an hallaka Maikasuwa ne lokacin da dakarun suke sintiri a ƙaramar hukumar Chikun.

An kama mutum 600 a Chadi saboda ‘shiga zanga-zanga’

Advertisement

Sanarwar ta ce jami’an tsaron sun samu nasarar ƙwato bindiga ɗaya ƙirar AK-47, da alburusai, da babura biyu da kuma kayan sojoji.

 

Advertisement

Ta ƙara da cewar Dogo Maikasuwa, wanda ake kira da Maimillion ya jagoranci kai hare-hare da garkuwa da mutane masu bin hanyar Kaduna zuwa Kachia da kuma wasu kauyuka na ƙaramar hukumar Chikun.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending