Connect with us

News

Yadda Aka Cafke Dan Bindiga Yayin Kai Hari A Kaduna

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Dubun wani dan bindiga ta cika bayan musayar wuta a kauyen Madugu da ke babbar hanyar Galadimawa zuwa Tumburtu da ke Karamar Hukumar Giwa ta Jihar Kaduna.

Advertisement

 

’Yan sanda sun cafke dan bindigar ne a ranar Alhamis, sannan suka kwace babura biyar na abokan ta’addancinsa da suka tsere bayan sun sha luguden wuta.

Advertisement

 

Shugaba Buhari ya amince da yi wa ma’aikatan shari’a ƙarin albashi

Kakakin ’yan sanda ta Jihar Kaduna, ASP Muhammad Jalige, ya ce bayan samun rahotanni kan ayyukan bata-garin a hanyar ne aka tura jami’ai daga rundunar Operation Whirl Punch suka fatattake su, kamar yanda jaridar aminiya ta rawaito

Advertisement

 

Ya ce bayan musayar wutar, ’yan bindigar sun tsere bayan yawancinsu sun samu raunukan harbi, suka bar baburansu guda biyar, amma an kama mutum daya daga cikinsu.

Advertisement

 

Ya ce a lokacin da suke masa tambayoyi, wanda ake zargin ya amsa cewa shi dan bindiga ne, kuma an kai kayan da aka kwace a hannunsu zuwa ofishin ’yan sanda domin ci gaba da bincike.

Advertisement

 

Jalige ya kuma shawarci mutanen yankin da su kai wa jami’an tsaro rahoton duk wanda suka gani da raunin harbi.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending