Connect with us

News

Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 17 Harin Ramuwar Gayya A Kauyen Kaduna

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wasu gungun ’yan bindiga sun kai hari a kauyen Rafin Sarki na gundumar Fatika da ke Karamar Hukumar Giwa ta jihar Kaduna, inda suka halaka mutum 17.

 

Advertisement

Shaidar gani da ido ta ta tabbatar wa Aminiya cewa harin an kai shi ne wajen misalin karfe hudu zuwa biyar na yammacin Alhamis.

 

Advertisement

An sace kayan fitar angwanci na wani ango a Kano

Majiyar ta kara da cewa maharan sun isa kauyen ne dauke da muggan makamai inda suka yi ta harbin kan mai uwa da wabi, inda suka kashe jama’a da dama, musamman wadanda ke gonakinsu a wannan lokaci.

 

Advertisement

Majiyar har ila yau ta ce ga dukkan alamu maharan sun je daukar fansa ne saboda sun dade suna kokarin kawo farmaki a kauyen amma garin ya gagare su shiga sakamakon dagewar da matasan yankin suka yi.

 

Advertisement

A cewar majiyar, “Wannan ya sa suka yi amfani da ranar ta Alhamis domin ita ce ranar kasuwar Giwa, sa’ilin da yawancin dakarun kauye suka tafi cin kasuwa sai suka afka wa garin.

 

Advertisement

“Yanzu haka, gawarwaki 17 muka gano kuma muka yi masu suttura. Amma kuma muna ci gaba da neman sauran jama’a da yawa wanda tun da abin ya faru har yanzu ba mu gansu ba.

 

Advertisement

“Babu rahoton sace shanu ko dabbobi ko wata kone-kone, illa rashin rayuka kawai bayan harin yan taaddar,” inji majiyar.

 

Advertisement

Duk kokarin neman Kakakin Rundunar ’Yan Sanda na jihar Kaduna, Mohammed Jalige ta waya kan harin ya gagara saboda lambarsa ta ki shiga har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending