Connect with us

News

Likita Daya Ne Ke Duba Marasa Lafiya 10,000 A Najeriya

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kungiyar Likitoci Masu Neman Kwarewa ta Najeriya (NARD) ta ce karancin likitocin da ake fuskanta a kasar ya yi munin da a yanzu likita daya ne ke duba marasa lafiya 10,000.

 

Advertisement

Kungiyar ta ce a halin da ake ciki, likitocin da ake da su a fadin kasar nan ba su wuce 10,000 ba.

Sulhu ne kadai zai iya magance yakin Ukraine- Macron

Ta ce adadin likitocin raguwa yake kullum sakamakon barin kasar da suke yi zuwa aiki a kasashen waje.

Advertisement

 

Shugaban kungiyar na kasa, Dokta Emeka Orji, ne ya bayyana haka yayin wata tattaunawa da jaridar Punch.

Advertisement

 

A cewarsa, kimanin likitoci 100 ne ke barin kasar zuwa ketare duk wata don neman aiki.

Advertisement

 

Ya ce, daga cikin likitoci 80,000 da suka yi rajista, kimanin kaso 64 cikin 100 ba sa aiki saboda wasunsu sun yi murabus, wasu sun bar kasar, wasu sun sake aiki, wasu kuma sun mutu.

Advertisement

 

Shugaban ya kuma ce kafin wannan lokacin, “Likitoci 16,000 ake da su, amma yanzu ba su wuce dubu tara zuwa 10 ba.”

Advertisement

 

Hakan na nufin likitocin da ake da su da za su kula da al’ummar Najeriya su sama da miliyan 200, ba su wuce guda 10,000 ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending