Connect with us

News

Tsohon Shugaban China, Jiang Zemin, Ya Rasu

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

 

 

 

Rahotanni daga kasar China sun ce tsohon Shugaban Kasar, Jiang Zemin, ya rasu.

Advertisement

 

Jiang ya rasu ne a Shanghai ranar Laraba, inda ya bar duniya yana da shekara 96.

 

Likita Daya Ne Ke Duba Marasa Lafiya 10,000 A Najeriya

Sanarwar rasuwar marigayin na kunshe ne cikin wata wasikar hadin gwiwa tsakanin hukumomin kasar da kuma babbar jam’iyyar kasar suka fitar.

 

Wasikar ta nuna yadda dukkan wadanda wasikar ta shafa suka mika ta’aziyyarsu ga al’ummar China dangane da rasuwar tsohon Shugaban.

Advertisement

 

Kazalika, wasikar ta nuna marigayin a halin rayuwarsa, shugaba ne tsayayye kuma mai kima a idon duniya wanda ya kasance abin so ga daukacin al’ummar kasar.

 

Ta kuma bayyana matuwarsa a matsayin babban rashi ga kasar baki daya.

 

(NAN)

Advertisement

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending