Connect with us

News

Kotun Amurka na tuhumar ɗan Mauritania da kisan Turawa a Mali

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAH 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wata kotu a birnin New York na Amurka na tuhumar wani mutum ɗan ƙasar Mauritania da laifukan ta’addanci da ke da alaƙa da wasu hare-hare da ya kai kan Turawan Yamma a ƙasar Mali a 2015.

 

Advertisement

Mutum 38 aka kashe a harin, ɗaya daga cikinsu Ba’Amurke ne.

Kwamitin Gudaji Kazaure haramtacce ne, ba Shugaba Buhari ya kafa shi ba – Garba Shehu

An gurfanar da Fawaz Ould Ahmed kwana ɗaya bayan da aka tasa ƙeyarsa daga Mali inda a nan ma aka yanke masa hukuncin kisa bayan amincewa da laifinsa.

Advertisement

 

Ya shaida wa kotu a Mali cewa ya kai harin ne domin ɗaukar fansa kan zanen ɓatanci da mujallar nan ta Charlie Hebdo ta yi kan Annabi Muhammad Salallahu Alaihi Wasallam.

Advertisement

 

BBC ta rawaito cewarsa, ko kaɗan ba ya nadama kan irin hare-hare da ya kai a wuraren shan barasa da otel-otel waɗanda baƙin Turawa kan sauka a Mali.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending