Connect with us

News

Kwamitin Gudaji Kazaure haramtacce ne, ba Shugaba Buhari ya kafa shi ba – Garba Shehu

Published

on

Garba Shehu

 DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

A Najeriya, fadar shugaban kasar ta mayar da martani kan wani ikirari da kwamiti na musamman da shugaban kasar ya kafa domin ya gudunar da bincike a kan cajin cirewa da ajiyar kudi a asusun banki.

Gwamnatin Najeriya na shirin rufe sansanonin ‘yan gudun hijira a fadin ƙasar

Shugaban kwamitin, Gudaji Kazaure ya yi zargin cewa wasu hukumomin da binciken ya shafa suna kokarin hana ruwa gudu game da aikin nasa, da kuma hana shi ya mika wa shugaba Muhammadu Buhari rahotonsa.

A cewar kwamitin wanda aka dora masa alhakin binciken cajin kudin ajiya da cire kudin tun daga shekara ta 2013 zuwa yanzu, ya gano cewa babban bankin kasar ya tara fiye da naira tiriliyon tamanin, amma ya yi zargin cewa ana sama da fadi da kudin.

Malam Garba Shehu, shi ne mai magana da yawun shugaban kasar Najeriya ya yi karin bayanin kan wannan batun ga BBC.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending