News
Sojojin Ukraine sun zargi jirage mara matuki na Iran da kai hari tashar lantarki ta Odesa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Sojojin Ukraine sun ce cikin awa 24 da ta wuce, an ga jiragen Iran marasa matuki 15 suna kai hari kan tashar lantarki a yankunan Odesa da Mikolaiv da ke kudancin kasar.
BBC ta rawaito cewa An dai kakkabo 10 daga cikin jiragen.
An kuma kai wasu hare-hare 15 kan sansanin sojin Ukraine, yankunan fararen hulda da tashohin lantarki sun fuskanci hare-haren roka a dama.
An kai harin atilare a yankin gabashi, sai dai har yanzu dakarun Rasha sun gaza kutsawa yankin.
Advertisements
