News
Yan Tunisiya na zanga-zangar neman shugaba Kais Saied ya sauka daga mulki
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Daruruwan masu zanga-zanga ne suka mamaye titin da ke Tunis babban birnin kasar, suna kira da shugaba Kais Saied ya sauka daga mukaminsa.
Zanga-zangar na zuwa ne mako guda gabanin zabukan da za su kai yin sauye-sauye ga kundin tsarin mulkin shugaba Saied, wanda ake ganin zai samar da majalisar jeka na yi ka.
An yanke wa attajiri Jimmy Lai hukuncin daurin kusan shekaru 6 a gidan yari
Wakilin BBC ya ce ‘yan adawa na zargin shugaban da kitsa wani abu mai kama da juyin mulki a watan Yulin 2021, inda ya kori manyan jami’an gwamnati ya kuma ruguje majalisar dokokin kasar, kuma tun daga nan yake aiki da dokar soji.
Tunisia na fuskantar matsaloli da dama da suka hada da na tabarbarewar tattalin arziki da gurguncewar siyasa da hauhawar farashin kayayyaki da dai sauransu.
