Connect with us

News

Babu hannuna a kisan kiyashin 2009 – Moussa Dadis Camara

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

Tsohon shugaban mulkin soja na Guinea Moussa Dadis Camara, ya musanta hannunsa a kisan kiyashin da jami’an tsaro suka yi a shekara ta 2009.

 

Advertisement

Ana tuhumar sa tare da wasu tsoffin jami’an soji da na gwamnati 10 kan kisan mutane sama da dari da hamsin da kuma yi wa mata fiye da dari fyade.

Mutum uku sun mutu bayan ‘yan bindiga sun kai hari a ofishin INEC da ke Imo

Hakan ya faru ne a cikin wani filin wasan kwallon kafa inda ‘yan adawa ke kokarin gudanar da gangamin siyasa.

 

Ana tuhumar Mista Camara ne da laifin daukar nauyin wadanda suka aikata mummunan laifin.

 

An soma shari’ar kisan kiyashin a watan Satumba, kuma bayyanar Camara wani muhimmin abu ne ga wadanda suka tsira da rayukansu da kuma dangin wadanda aka kashe

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending