Connect with us

News

Hisbah Ta Cafke Matasa 19 Kan Kokarin Shirya Auren Jinsi Daya A Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wasu matasa 19 sun shiga hannun Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, kan kokarin hada auren jinsi daya a jihar.

 

Advertisement

Wadanda suka shiga hannun, da yawansu matasa ne sun yi kokarin daura wa wasu maza biyu masu suna Abba da Mujahid aure a matsayin miji da mata.

Ummita: Rashin Shaida Ya Kawo Tsaiko A Shari’ar Dan China

 

Advertisement

Jami’an hukumar sun yi wa wajen da za a daura auren dirar mikiya, inda suka damke mata 15 da kuma maza hudu.

 

Advertisement

Da yake tabbatar da kamen matasan, Babban Kwamandan hukumar, Sheikh Haruna Ibn Sina, ya ce amarya da angon (Abba da Mujahid) sun tsere bayan da jami’an Hisbah suka dira wajen.

 

Advertisement

 

Sai dai Ibn Sina ya ce wadda ta shirya bikin, Salma mai shekara 21 na hannun hukumar.

Advertisement

 

Amma ya ce hukumar na ci gaba da samamen wadanda suka tsere din don ta kama su.

Advertisement

 

Kwamandan ya ce tuni hukumar ta nutsa da bincike don gurfanar da wadanda suka shiga hannunta, wanda a cewar wasu daga cikinsu gayyatarsu aka yi zuwa wajen daurin auren.

Advertisement

 

Amma ya ce wasu daga cikin wadanda aka kama din sun roki da a yi musu sassauci bisa sharadin ba za su sake aikata laifin ba.

Advertisement

 

 

Advertisement

Auren Jinsi

bincike

Advertisement

Hisbah

kano

Advertisement

matasa

Karin

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending