News
Jam’iyya mai mulki a Jamhuriyar Nijar PNDS-Tarayya ta zabi sabon shugaba
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jam’iyyar Party for Democracy and Socialism PNDS-Tarayya da ke mulki a Jamhuriyar Nijar ta zabi Foumakoye Gado a matsayin sabon shugabanta.
An gudanar da zaben ne ranar Lahadin da ta gabata, bayan an kwashe kwana biyu ana taron jam’iyyar a Tahoua.
Bala’in sanyi ya sa mutane sun kasa fita daga motocinsu a Amurka
Foumakoye Gado ya maye gurbin Mohamed Bazoum, wanda shi ke shugabancinta kafin ya zama shugaban kasar.
Tsohon ministan ya zama shugaba na uku na jam’iyyar PNDS bayan tsohon Mahamadou Issoufou da shugaban shugaban kasa mai-ci.
Foumakoye Gado ya rike mukamin mataimakin shugaban jam’iyyar tun daga 2013.
Advertisements
