Connect with us

News

Ɗaliban jami’o’i a Ghana sun koka kan ƙarin kuɗin makaranta

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Ɗaliban jami’o’i a ƙasar Ghana sun yi watsi da ƙarin kuɗin makaranta da wasu jami’o’in ƙasar suka yi.

Advertisement

 

Ƙungiyar Daliban ƙasar ta umarci masu ruwa da tsaki da su hana jami’o’in ƙasar ƙara kuɗin makarantar.

Advertisement

Gwamnan Legas ya gana da sifeton ‘yan sanda kan kisan lauya

A baya-bayan nan ne dai Majalisar Dokokin ƙasar ta amince da ƙarin kashi 15 cikin 100 na kuɗin makaranta ga jami’o’in ƙasar.

 

Advertisement

To sai dai ɗaliban na cewa wasu jami’o’in sun yi ƙarin kusan kashi 40 cikin 100, saɓanin abin da majalisar dokokin ƙasar ta amince da shi.

 

Advertisement

Daliban sun bayyana damuwarsu game da lamarin, yayin da ƙasar ke fama da tsadar rayuwa, da ƙaruwar farashin kayyaki da kusan kashi 50 cikin 100.

 

Advertisement

Ƙungiyoyin ɗaliban ƙasar sun ce ƙarin kuɗin zai jefa dalibai da iyayensu cikin mawuyacin hali.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending