Connect with us

News

China na ɓoye ainihin alkaluman cutar korona – WHO

Published

on

DAGA HASSAN KHALID HAMZA

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, ta yi gargadin cewa China na ɓoye ainihin tasirin da annobar korona ta yi wa ƙasar – musamman ma alkaluman wadanda suka mutu.

 

Advertisement

Cire yawancin takunkumai da ƙasar ta yi a watan da ya gabata, ya janyo ƙaruwar mutane masu kamuwa da cutar.

An dakatar da Lewandowski wasa uku jere a La Liga

Sai dai China ta daina wallafa alkaluman masu cutar a kowace rana, inda ta sanar da cewa mutum 22 ne kadai suka mutu sakamakon korona tun watan Disamba.

Advertisement

 

Darektan bayar da agajin gaggawa na hukumar, Dr Michael Ryan, ya ce abin da suke gani a China kan cutar korona ba shi ne ainihin abin da yake faruwa ba musamman idan aka duba wadanda ake kwantar wa a asibiti da ke bukatar kulawar gaggawa da kuma wadanda ke mutuwa sanadin cutar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending