News
Sanyi: An samu gawar mata da miji a kulle a daki a nan Kano.
DAGA YASIR SANI ABDULLAH
An samu Sulaiman Idris, Dan shekara 28 da matar sa Maimuna Hallilu mai shekaru, 20 a mace a kan gadon su na aure.
Premier radio ta rawaito cewa Lamarin ya faru ne karamar hukumar Dawakin Tofa a nan Kano a ranar Litinin.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda na Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar Laraba.
DSS Ta Cafke Mutum 2 Kan Zargin Tayar Da Bam Yayin Ziyarar Buhari Jihar Kogi
Ya ce an gano ma’auratan basu fito daga dakin su ba tun a ranar Litinin da karfe 11 na safe.
Kiyawa, ya ce ofishin su dake kauyen Kwa a karamar hukumar Dawakin Tofa, ya karbi korafi a ranar Talata dake cewa wasu ma’aurata Sulaiman Idris da matar sa Maimuna basu fito daga dakin su ba tun ranar Litinin.
Bayan yin bincike an gano ma’auratan sun kunna gawayi don dumama dakin su saboda sanyi inda suka kulle suka kwanta bacci, Wanda hayakin gawayin yayi sanadiyar mutuwar su.
Ya kara da cewa yayin da kakar mijin ta tura kofar dakin ta same su yashe akan gado da kuma warin hayakin gawayin da ya cika dakin.
SP Kiyawa ya Kuma ce bayan samun rahoton ne jami’an su suka garzaya inda suka dauki gawarwakin zuwa asibitin Muratala inda a nan ne likita ya tabbatar da mutuwar su.
SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce kwamishinan ‘yan sanda na Kano ya shawarci al’umma da su rinka lura wajen yin amfani da wuta a lokacin sanyi.
