News
Kotu a Legas ta tura likita gidan yari bisa zargin yin lalata da ‘yar shekara 16
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wata kotun sauraron kararraki kan laifuka na musanman da keta mutuncin yara ƙanana ta jihar Legas, ta tura wani babban likita gidan yari, bisa zarginsa da yin lalata ta baki da wata yarinya ‘yar shekara goma sha shida.
An gabatar da Dokta Olufemi Olaleye, manajan daraktan cibiyar gidauniyar kula da masu cutar daji, a gaban kotu; to sai dai a tsawon zaman ya musanta zargin da ake yi ma sa.
Advertisements
