Sports
Madrid ta ɓarar da damar hawa teburin Laliga bayan shan kashi a hannun Villareal
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta ɓarar da damar hawa teburin gasar Laliga bayan doke ta da ci 2-1 da Villareal ta yi a wasan mako na 16.
Villareal ce ta fara cin kwallo ta hannun ɗan wasan ta Yeremy Pino mintuna ƙaɗan bayan dawowa daga hutun rabin lokaci.
Sai dai Madrid ta samu nasarar farke kwallon ta hannun Karim Benzema a bugun fenariti ana minti 60.
Daga bisani ne kuma ɗan wasan Villareal Gerard Moreno ya saka su a gaba a bugun daga fenariti bayan da kwallo ta daki hannun dan wasan bayan na Real Madrid, David Alaba.
Wannan sakamako na nufin har yanzu Madrid na a mataki biyu ne na teburin gasar Laliga maƙi ɗaya da Barcelona wadanda za su fafata da Atletico Madrid a gobe Lahadi.
-
News1 day ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
