Connect with us

News

BABBAR MAGANA:Fasto Ya Sace Kansa Ya Karbi Kudin Fansa Daga Mabiyansa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Rundunar ’yan sandan jihar Filatu ta cika hannunta da wani fasto da ake zargi da karyar an sace shi, ya kuma karbi kudin fansa daga mabiyansa.

 

Advertisement

Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Alabo Alfred, ya fitar ranar Laraba a Jos, ya ce an kama faston ne tare da wasu mutane uku da ya hada baki da su a matsayin wadanda suka sace shi.

 

Advertisement

Ana Bincike Akan Mijin Da Ya Kashe Matarsa Kan Burodi

 

 

Advertisement

“Sau biyu yana yin haka da sunan an sace shi. A ranar 14/11/2022, da kuma 30/11/2022 ne mabiyansa suka biya N400,000 da kuma N200,000 a matsayin kudin fansa a lokuta daban-daban, daga nan ne ma suka fara tantamar lamarin.

 

Advertisement

“Da zancen ya zo gabanmu muka shiga bincike, muka gano ashe hada baki ya yi da wasu matasa uku, da ke boye shi, da kuma yin magana a matsayin wadanda suka sace shi.

 

Advertisement

 

“Baya ga haka, ya kuma fada mana ya taba kone motar wani shugabansa a coci ranar 4/1/2023, saboda ya fahimci baya kaunarsa,” in ji shi.

Advertisement

 

Jami’in ya ce faston da mutum biyu daga cikin abokan cin mushensa suna hannu, guda ya ari na kare, kuma da zarar sun kamo shi za su gurfanar da su a gabana kotu.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending