Sports
Kotu ta tisa keyar Dan wasan Brazil Dani Alves zuwa gidan yari.
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Wata kotu a ƙasar Sifaniya ta bayar da umarnin tsare ɗan wasan Brazil Dani Alves a gidan yari har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci a kan shari’ar da ake yi masa kan zargin cin zarafin wata mata.
A ranar Juma’a ne aka tsare ɗan wasan mai shekara 39 a birnin Barcelona.
Kada ‘yan Najeriya su ɗaga hankulansu kan ɓarkewar cutar mashaƙo – NCDC
Alves wanda tsohon ɗan wasan Barcelona ne ya musanta zargin cewa ya ci zarafin wata mata a wani gidan rawa.
Kan wannan batun dai tuni ƙungiyar da ɗan wasan ke taka wa leda Pumas UNAM ta ƙasar Mexico, ta ce ta soke kwantiragin ɗan wasan nan take.
Advertisements
