News
Ana tuhumar yaro ɗan shekara 13 da fyaɗe da cin zarafin mata
DAGA MARYAM BASHIR MUSA
Wani yaro ɗan shekara 13 zai fuskanci tuhuma kan cin zarafin mata da yara mata a Telford.
Ƴan sanda sun ce sau biyar suna samun rahoto tsakanin 15 ga watan Disamba 2022 zuwa 19 ga watan Janairun, cewa ana yawan kai wa mata manya da kuma ƙanana tsakanin shekara 16 zuwa 34 hari a yankunan Hadley Leegomery.
Ana tuhumar yaron da aikata laifukan cin zarafi ta hanyar lalata har sau tara, ƙoƙarin fyade sau biyu da kuma cin zarafi har da duka sau biyu.
Ya bayyana a gaban kotun matasa ta Kidderminster a ranar Laraba, kuma yanzu yana tsare a ƙarƙashin kular hukumomi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
