News
Barazanar Kisa: Kotu Ta Sa A Cafke Shugaban APC Na Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kotu ta ba da umarnin tsare Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Abdullahi Abbas, da kuma gurfanar da shi a gaban kuliya kan zargin barazanar kisa.
Babbar Kotun tarayya da ke zama a Kano ce ta sa a tsare, a bincika da kuma gurfanar da Abdullahi Abbas, kan zargin barazanar kisa, tayar da zaune tsaye da kuma kalaman tsana, ga Mahmoud Lamido.
‘Yan sanda sun gurfanar da wani mutum a Kotu da laifin ya ƙara aure.
Mahmoud Lamido ya shaida wa kotun ta bakin lauyansa cewa shugaban jam’iyyar ya kira shi a waya yana barazana ga rayuwar sa da cewa, “Sai na batar da kai.”
Akalin koun, Mai Shari’a S.A Amobeda, ya dage sauraron karar zuwa ranar 16 ga Fabairun da muke ciki domin ’yan sanda su aiwatar da umarnin.
Jam’iyyar NNPP ta bayyana umarnin kotun da cewa babbar nasara ce ga tafiyar dimokuradiyya a Jihar Kano.
Kakakin kwamitin yakin neman zaben NNPP na jihar, Sunusi Bature ya yi zargin irin kalaman Abdullahi Abbas na iya kawo yamutsi.
A cewarsa, karo na biyu ke nan kotu na umartar Kwamishinan ’yan sandan Jihar Kano ya tsare shugaban APC na jihar.
Kawo yanzu dai ba a ji uffan daga bangaren APC ko rundunar ’yan sandan jihar Kano ba.
