Connect with us

News

Girgizar ƙasar Turkiyya da Syria: Sama da mutum 28,000 sun mutu

Published

on

 

 

Advertisement

 

Adadin mutanen da suka mutu sakamakon bala’in girgizar ƙasar da ya afka wa ƙasashen Turkiyya da Siriya ya zarta 28,000, yayin da ake ci gaba da aikin ceto.

Advertisement

 

To sai dai fatan samun ƙarin masu numfashi na gamuwa da cikas yayin da ake samun rahotonnin rashin zaman lafiya a wasu yankunan kudancin Turkiyya, lamarin da ke yin barazana ga masu aikin ceton kamar yadda wasu ƙungiyoyin agaji uku suka bayyana..

Advertisement

Sojojin Najeriya Na Fatattakar Yan Boko Haram a Dajin Sambisa

Ƙungiyar agaji ta ƙasar Jamus da takwararta ta ƙasar Austria sun dakatar da ayyukansu ranar Asabar, sakamakon abin da suka kira rikici tsakanin wasu ƙungiyoyi a yankin.

 

Advertisement

Wani jami’in ceto ya ce ana fargabar ƙaruwar tabarɓarewar tsaro, yayin da jigilar kayan abinci zuwa yankin ke gamuwa da cikas.

 

Advertisement

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce zai yi amfani da ƙarfi wajen ladabtar da duk wanda yake ƙoƙarin karya doka.

 

Advertisement

Aƙalla gidaje 6,000 ne suka rushe a Turkiyya, lamarin da ke ɗiga ayar tambaya game gwamnatin Recep Tayyip Erdogan za ta iya yin abin da ya kamata domin kare rayuka.

 

Advertisement

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana girgizar ƙasar da ‘mummunan bala’in’ da yankin ya taɓa gani cikin shekarar 100.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending