Connect with us

News

Kotu Ta Daure Matashin Da Ya Karya Kafar Dan Sanda A Kano

Published

on

 

 

Advertisement

Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Unguwar Kwana Hudu da ke Jihar Kano, ta yanke wa wani matashi hukuncin daurin watanni 6 a gidan gyaran hali bisa samunsa da karya kafar wani dan sanda.

 

Advertisement

Tun da farko an tuhumi matashin mai suna Umar Usaini Birnin Kudu da laifin karya kafar wani jami’in dan sanda a Karamar Hukumar Takai ta Jihar Kano.

Zargin cin zarafin Naira:Kotu ta bayar da belin Jarumar noollywood a kan miliyan 5

 

Advertisement

Lamarin ya faru ne yayin da jami’in dan sandan ya ziyarci matashin domin sanar da shi cewa an yi korafi a kansa a ofishin ’yan sanda na garin Takai.

 

Advertisement

Wakiliyarmu ta ruwaito cewa, matashin ya karya karfa dan sandan guda daya yayin da yake kokarin guduwa.

 

Advertisement

Bayan cafke shi ne aka gurfanar da shi a gaban kotun inda kuma ya amsa zargin da ake yi masa.

 

Advertisement

Mai gabatar da kara a gaban kotun, Aliyu Abidin Murtala ya roki kotun da ta yi masa hukunci bisa ikirarin bakinsa.

 

Advertisement

Alkalin kotun, mai shari’a Mallam Nura Yusuf Ahmad, ya yanke masa daurin watanni 6 a gidan gyaran hali ba tare da zabin biyan tara ba.

 

Advertisement

Kazalika, kotun ta yanke cewa matashin zai biya kudin dori da magani har Naira dubu dari da arba’in da uku da dari biyar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending