Connect with us

News

Soja Ya Harbe Dan Siyasa A Cibiyar Tattara Sakamakon Zabe

Published

on

 

 

Advertisement

 

Wani soja ya harbe wani jigon Jam’iyyar PDP, Akinlabi Akinnaso, har lahira a Karamar Hukumar Idanre da ke Jihar Ondo.

Advertisement

 

Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, inda daya daga sojojin da aka tura samar da tsaro a cibiyar tattara sakamakon zabe a yankin ya harbi margayin bisa kuskure.

Advertisement

 

Babu Tabbacin Ba Za A Iya Yi Wa Rumbun Adana Bayanan INEC Kutse Ba – Jega

Majiyarmu ta ce hakan ta faru ne a lokacin da marigayin ya raka dan takararsu na Majalisar Wakilai da ya lashe zabe don karbar takardar shaidarsa a wajen INEC.

Advertisement

 

“Mun taru a cibiyar tattara sakamakon zabe muna jiran takardar shaidar lashe zabe ta dan takarnmu, Honorabul Akingbaso, a nan sojoji suka fara korar mu daga cibiyar don rage cunkoso.

Advertisement

 

 

Advertisement

“Bayan mun yi nesa da cibiyar, can sai muka hangi Akinnaso ya doshi cibiyar don ya cim mana alhali bai san abin da ke faruwa ba.

 

Advertisement

“Amma ko da ya yi kusa da sojojin sai muka ga ya fadi bayan da aka harbe shi.

 

Advertisement

“Bayan da muka dauke shi zuwa asibiti, aka tabbatar mana ya mutu,” in ji majiyar.

 

Advertisement

Da aka nemi jin ta bakin kakakin ’yan sandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisanya, ta ce ba ta da cikakken bayani kan abin da ya faru.

 

Advertisement

 

Ta yi alkawarin za ta yi magana da zarar ta samu cikakken bayani kana bin da ya faru.

Advertisement

 

Aminiya

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending