News
INEC ta ce babu wanda ya ci zabe a mazabar Doguwa
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa babu wanda ya lashe zaben ‘yan majalisar tarayya da aka gudanar a mazabar Doguwa da Tudunwada a ranar 25 ga watan Fabrairu.
Da farko dai an bayyana shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai Alhassan Doguwa wanda da tsaya takara a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a matsayin wanda ya lashe zaben.
Matashi ya halaka abokin takarar sa a wajen budurwa Jihar Adamawa
Sai dai alkalan zaben ya cire sunansa daga cikin wadanda aka zaba kuma ya kasa ba shi takardar shaidar cin zabe.
Hukumar dai ta ce an tilasta shi ne a matsayin wanda ya lashe zaben.
Hakan ya biyo bayan kame Doguwa da aka yi dangane da rikicin da ya barke a mazabar yayin da ake gudanar da zaben.
Akalla mutane biyu ne suka mutu lokacin da aka kona sakatariyar jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP) a yankin.
Rundunar ‘yan sandan ta gurfanar da babban dan majalisar a gaban wata kotun majistare wadda ta tura shi gidan yari.
Amma Doguwa an bayar da belin Naira miliyan 500
Daily Trust
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
