Connect with us

News

INEC ta ce babu wanda ya ci zabe a mazabar Doguwa

Published

on

 

 

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa babu wanda ya lashe zaben ‘yan majalisar tarayya da aka gudanar a mazabar Doguwa da Tudunwada a ranar 25 ga watan Fabrairu.

 

Da farko dai an bayyana shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai Alhassan Doguwa wanda da  tsaya takara a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a matsayin wanda ya lashe zaben.

Matashi ya halaka abokin takarar sa a wajen budurwa  Jihar Adamawa

Sai dai alkalan zaben ya cire sunansa daga cikin wadanda aka zaba kuma ya kasa ba shi takardar shaidar cin zabe.

Advertisement

Hukumar dai ta ce an tilasta shi ne a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hakan ya biyo bayan kame Doguwa da aka yi dangane da rikicin da ya barke a mazabar yayin da ake gudanar da zaben.

Akalla mutane biyu ne suka mutu lokacin da aka kona sakatariyar jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP) a yankin.

Rundunar ‘yan sandan ta gurfanar da babban dan majalisar a gaban wata kotun majistare wadda ta tura shi gidan yari.

Amma Doguwa an bayar da belin Naira miliyan 500

 

Advertisement

 

Daily Trust

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending