News
Rikicin : Mutum 6 Za Su Fuskanci Hukunci A Legas
Rundunar ’yan sandan Jihar Legas, ta ce nan ba da jimawa ba za ta gurfanar da mutum shida daga cikin 19 da ake zargi da aikata laifukan zabe a Jihar.
Ana dai zargin mutanen ne da aikata laifukan yayin zaben gwamnoni da na ’yan majalisar dokokin jihar da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata.
Majalisa Za Ta Binciki Musabbabin Yawan Hatsarin Jirgin Kasa A Najeriya
Rundunar ta kuma ce ta gano dimbin katunan zabe da wasu da ake zargin ’yan bangar siyasa ne suka jefar a wurare daban-daban a jihar.
Rundunar ta ce an jefar da katinan zaben da aka kwato sannan aka yi waje da su domin tserewa.
Kakakin rundunar a Jihar, SP Benjamin Hundeyin, da yake gabatar da wadanda ake zargin a ranar Talata a sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID), da ke titin Panti, Yaba, ya ce wadanda aka kama suna da hannu a laifuka 21 da suka hada da kai hari kan jami’an INEC da lalata kwace akwatin zabe.
Ya ce za a kuma gurfanar da wadanda don zartar musu da hukunci.
Ya ce hudu daga cikin wadanda ake zargin za a gurfanar da su a gaban hukumar zabe ta INEC, yayin da biyu da aka samu da makamai da kuma aikata wasu laifuka za a gurfanar da su a gaban kotu.
Hundeyin ya kara da cewa wasu mutane uku daga cikin wadanda aka kama sun kuma amsa laifin yin garkuwa da su tare da karbar kudin fansa kimanin Naira miliyan 20.7 daga hannun wadanda abin ya shafa.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
