News
Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kano ta sanar da haramta wasan tashe a watan Ramadan a kwaryar birnin Kano.
Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kano ta sanar da haramta wasan tashe a watan Ramadan a kwaryar birnin Kano.
A bisa al’ada, a kan fara wasan tashe ne daga 10 ga watan azumin har zuwa karshensa, inda mutane kan yi wasa iri-iri yayain da mutane kuma ke ba su kyaututtuka.
To sai dai a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta bakin Kakakinta, Abdullahi Haruna Kiyawa, ta ce an haramta al’adar ce a bana, kamar bara ma, saboda fargabar samun rikici.
Ya ce sun dauki matakin ne saboda yadda bata-gari ke fakewa da dadaddiyar al’adar wajen aikata laifuka irin su daba kwacen waya, shaye-shaye da sauransu
Ya sha alwashin jami’ansu za su kama duk wanda aka samu ya yi kunnen uwar shegu da dokar.
Kazalika, rundunar ta ce har yanzu haramcin da ta sanya a kan yin kilisar dawakai ba bisa ka’ida da kuma yin wasan tartsatsin wuta ko fasa naka-awut lokacin bukukuwa na nan daram.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News4 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
