News
Kungiyar Shugabannin Kananan Hukumomin Najeriya (ALGON) Ta Gargadi Kwamitin Abba Kan Zafafa Siyasa
Kungiyar Shugabannin Kananan Kwamitin Karbar Mulki na Jam’iyyar NNPP da ya daina zafafa siyasa da haifar da tashin hankali ko furta lafuzan da ka iya haifar da hargitsi.
Shugaban ALGON na jihar Kano, Bappa Muhammad ya yi kiran ne a sanarwa da ya fitar, kan zargin karkatar da kudaden al’umma da kwamitin ke yi wa shugab kananan hukumomin jihar domin bayar da tallafin karashen zaben da ke tafe nan gaba.
A cikin makon nan ne dai shugaban kwamitin, Abdullahi Baffa Bichi ya gargadi shugabannin kananan hukumomin kan yin almubazarranci da dukiyar gwamnati.
Amma a martaninta kungiyar ta yi kira gare shi da ya yi aiki da hankali domin irin wannan tashin hankalin jama’a ba zai iya tasowa ba a wannan tafiyar ta dimokuradiyya.
“An saba yin irin wadannan zarge-zargen a duk lokacin da aka samu sauyin a shugabanci.
“Muna so musamman mu tunatar da mai yin wadannan zarge-zarge game irin hakan da aka yi wa tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dokta Rabi’u Musa Kwankwaso a shekarar 2014 na yin amfani da kudaden al’umma da ya karbo daga kananan hukumomi 44 da aka yi wa shugaban kasa buri.
“Idan dai za a iya tunawa dai an yi zargin an karbo makudan kudade har Naira miliyan saba’in daga kowacce daga cikin kananan hukumomi 44 da ke jihar ba bisa ka’ida ba, wanda har yanzu shari’ar tana gaban hukumomi, ta ki da cin hanci da rashawa’’.
A ranar 29 ga watan Mayu mai zuwa ne dai ake sa ran rantsar da Injiniya Abba Kabir Yusuf a matsayin sabon gwamnan jihar Kano.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
