News
Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Kudirin Gyaran Dokar Masarautun Jihar.
Majalisar dokokin Kano ta amince da kudirin gyaran dokar masarautu ta jihar Kano ta shekerar 2019.
Majalisar ta amince da gyaran a zaman ta na Talatar nan karkashin kakakinta Hamisu Ibrahim Chidari.
Jami’an bijilanti sun kama matasa guda 2 da ake zarginsu da satar ƙofofin jama’a watan Ramadana
Gyaran dai ya kunshi rage mambobin majalisar zartaswa ta sarakunan jihar Kano zuwa mutane goma sha bakwai maimakon mutane 25.
Haka kuma gyaran ya bayar da damar samar da gidajen da zasu iya gadar sarki koda Allah yayi wani sarki ya rasuwa daga cikin sarakunan Kano.
A wani cigaban kuma majalisar dokokin ta amince da sabon taken jihar Kano wanda za a rinka amfani dashi a guraren taruka a fadin jihar nan.
Gwamnatin Kano da jami’ar Bayero ne dai suka samar da taken na jihar Kano.
Majalisar ta kuma karbi takardar daga gwamnan Kano dake neman sahalewa domin samar da hukumar da zata rinka kula da tituna a yankunan karkara.
Haka kuma majalisar dokokin ta Kano ta kuma karbi takarda daga gwamnan Kano dake neman majalisar ta amince da Balarabe Hassan Karaye a matsayin kwamishina a hukumar zabe ta jihar Kano (KANSIEC).
Majalisar ta kuma dage zaman ta zuwa Larabar nan.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
