Connect with us

News

Karasa Zabe: Za Mu Samar Da Tsaro A Kano —’Yan Sanda

Published

on

 

Rundunar ‘Yan sandan Kano ta ba wa mazauna jihar tabbacin samun isasshen tsaro a yayin zaben da za a gudanar a ranar 15 ga watan Afrilu.

Advertisement

 

Kwamishinan ‘Yan sandan jihar, CP Mamman Dauda ne ya bayyana hakan yayin wani taron masu ruwa da tsaki kan zaben da za a karasa, wanda aka gudanar a ofishin INEC da ke Kano.

Advertisement

Gwamnati Ta Karrama Limamin Da Ya Tausasa Kyanwa Yana Jan Sallah

Mamman Dauda wanda Mataimakin kwamishinan ‘yan sanda mai kula da ayyuka, Mu’azu Mohammad, ya wakilta, ya ce tuni ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro a jihar suka tsara yadda yanayin tsaro zai kasance a ranar da nufin tabbatar da zabe cikin kwanciyar hankali.

 

Advertisement

CP Dauda ya ce ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro a jihar na kokarin ganin an gudanar da zabe ba tare da an samu wani rikici ba.

 

Advertisement

 

Ya bayyana cewa tuni aka ba da umarnin aiki kan yadda za a samar da tsaro a duk runfunan zabe ga jami’an da aka tura domin gudanar da aikin.

Advertisement

 

Kwamishinan ‘yan sandan ya shawarci shugabannin jam’iyyun siyasa da ‘yan takara da su gargadi magoya bayansu da su guji yin duk wani abu da zai kawo tashin hankali kafin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe.

Advertisement

 

A nasa bangaren, Kwamishinan Zabe na jihar, Ambassada Abdu Zango, ya ce duk da cewa an gudanar da zabukan Shugaban Kasa da na gwamnoni cikin kwanciyar hankali a Kano, wasu mazabu na Tarayya da na jiha an samu kalubalen da ya sa za’a sake zaben.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending