Connect with us

News

Gwamnati Ta Karrama Limamin Da Ya Tausasa Kyanwa Yana Jan Sallah

Published

on

Gwamnatin Aljeriya ta karrama Imam Walid Mehsas wanda kyanwa ta dare jikinsa a daidai lokacin da yake jagorantar Sallar Tarawih.

 

Advertisement

Limamin cikin tausasawa ya yi ta shafar kwanyar wadda ta sumbaci kuncinsa kafin ta sauka daga jikinsa don radin kanta.

 

Wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta ne ya nuna yadda Imam Walid ya mu’amalanci kwanyar cikin kyan yanayi, lamarin da ya kayatar da jama’a da dama hatta wadanda ba Musulmi ba daga sassan duniya.

Advertisement

 

Limamin ya sha yabo da jinjina, yayin da manyan kafafen yada labarai na duniya suka yi ta yada labarin.

Advertisement

 

 

Advertisement

Gwamnatin Aljeriya ta gayyace shi ta shirya masa liyafa ta musamman, inda Ministan Kula da Lamurran Addini na Kasar, Dokta Youssaf Belmahdi ya yaba masa kan wannan kyakkyawar dabi’ar da ya nuna wa dabba.

 

Advertisement

(rfi)

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending