News
Allah Ya yi wa daya daga cikin limaman Masallacin Manzon Allah (SAW) da ke Madina, rasuwa.
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Allah Ya yi wa Sheikh Muhammad Khaleel Al-Qari, daya daga cikin limaman Masallacin Manzon Allah (SAW) da ke Madina, rasuwa.
Kafin wayewar garin Litinin Allah Ya yi wa malamin rasuwa, kamar yadda Hukumar Gudanarwar Masallatan Harami da na Madina ta sanar ta shafinta.
Dangote Ya Bayyana Ranar Da Zai Kaddamar Da Kamfanin Matatan Mai.
Ta bayyana cewa za a gudanar da Sallar Jana’izar malamin da Magriba, idan Allah Ya kai mu.
Sheikh Muhammad Khaleel Al-Qari yana daga cikin limamai baki da ke jagoracin Sallar Tarawih a masallacin, da ke karbar bakuncin miliyoyin masu ziyara a duk shekara.
Advertisements
