News
Kotu ta Haramtawa NBC Cin Tarar Tashoshin Watsa Labarai
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta haramtawa hukumar kula da kafafen yada labarai ta kasa NBC cin tarar gidajen yada labarai a Najeriya, kamar yanda jaridar The Cable ta rawaito.
A hukuncin da ya yanke ranar Laraba, James Omotosho, shugaban alkalin kotun, ya ce hukumar NBC ba ta da hurumin yanke hukunci.
Alkalin ya yi watsi da tarar da NBC ta kakaba wa tashoshin watsa labarai 45 a ranar 1 ga watan Maris din shekarar 2019.
Advertisements
