Connect with us

News

Kungiyar ECOWAS ta sake yin kiran a murkushe ta’addancin da ke karuwa a tsakiyar Sahel

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

 

Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS) ta jaddada buƙatar a ɗauki matakan gaggawa domin magance ƙaruwar hare-haren ta’addanci a tsakiyar Sahel.

Advertisement

 

Kwamishinan ECOWAS da ke kula da harkokin siyasa da zaman lafiya da tsaro, Ambasada AbdelFateh Moussa ne ya yi wannan kira a wani taron bayar da horo na yini biyar.

Ya Kamata Sabuwar Gwamnati Ta Dauki Darasi Daga Kura-Kuran Da Gwamnatocin Baya Suka Tafka—-sunusi na biyu

An yi wa taron taken Tabbatar da ci gaban zaman lafiya: Rawar ƴan sanda da jami’an Jandarma wajen tafiyar da ayyukan ECOWAS wajen wanzar da zaman lafiya.

 

ECOWAS ce ta shirya taron haɗin gwiwa da kwalejin horas da ƙananan jami’an soji ta Najeriya tare da tallafin shirin ECOWAS kan zaman lafiya da tsaro.

 

Advertisement

Moussa ya ce ayyukan wanzar da zaman lafiya da aka saba na zama tsohon yayi saboda yanayin rikici a yankin.

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending