Connect with us

News

Rundunar Yan sanda Sun Kama Mutumin Da Yayi Yunkurin Bankawa Masallaci Wuta

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

 

‘Yan sanda sun kama wani mutum da ya yi yunkurin cinnawa wani masallaci wuta a birnin Dresden na Jamus da yammacin jiya Talata.

Advertisement

 

Jaridar post ta ruwaito cewa Mutumin ya zuzzuba fetur a kewayen wani masallaci tare da kokarin cinnawa ginin wuta, in ji kakakin ‘yan sandan.

 

Kungiyar ECOWAS ta sake yin kiran a murkushe ta’addancin da ke karuwa a tsakiyar Sahel

 

Shaidu gani da ido, sun kira lambar hukumar bayar da agajin gaggawa bayan da suka ga mutumin yana zuba mai a harabar masallacin, wanda a lokacin ya shiga hannu

 

Advertisement

An kama mutumin mai shekaru 34, kuma yana karkashin binciken ‘yan sanda kan yunkurin tada kayar baya.

 

Ko da yake da farko ba a san dalilinsa ba, amma an ce wanda ake zargin ya kona wani kwafin Alkur’ani mai girma a wani masallaci a watan Afrilun shekarar nan.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending