News
Majalisar Sakkwato Ta Kafa Dokar Hana Tsadar Aure
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Majalisar Dokokin Jihar Sakkwato ta sanya hannu kan wani kudirin dokar da ke sanya ido kan tsada da almubazzarancin da jama’a ke yi a bikin aure a jihar.
Kudirin wanda Alhaji Abubakar Shehu na jam’iyyar APC da Faruk Balle na jam’iyyar PDP suka gabatar, sai da aka fara gabatar da shi ga Kwamitin Kula da Al’amurran Addini a majalisar.
In Tinubu Ya Bani Minista Bazan Karba Ba Saboda Na Tsufa Da Yin Rushe-Rushe – El Rufa’i
Shehu wanda shi ne shugaban kwamitin, ya gabatar da rahotonsu a wani zaman farko na ‘yan majalisar kuma daukacinsu suka amince ya zama doka.
Kudirin dokar na bukatar sanya ido kan almubazzarancin kudi da ake yi a yayin bikin aure da taron suna da kaciya da sauran bukukuwa a sassan jihar.
Bayan wata muhawara a zaman na farko da Mataimakin Shugaban Majalisar ya jagoranta, Alhaji Abubakar Magaji, kudirin dokar ya samu amincewar ’yan majalisar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
