Daruruwan masu aikin tafinta ‘yan kasar Afghanistan wadanda suka yi wa sojojin Burtaniya aiki a Afghanista sun makale a otel-otel din kasar Pakistan har na tsawon watanni ko kuma ma sama da shekara ɗaya.
A ka’ida dai masu tafintan na da hurumin zama a Burtaniyar to amma gwamnatin ta dakatar da kwashesu da kuma iyalansu zuwa can tun watan Nuwamba inda suka ce babu isassun gidaje.
Yan Najeriya Sama Da Dubu 40 Ne Ke Mutuwa Kowacce Shekara Saboda Hadari
An dai fada mu su su jira sai wata shekarar.
A wani korafin da suka yi wa BBC, sun bayyana cewa ba za su iya barin otel-otel dinsu ba saboda bizarsu ta Pakistan ta mutu kuma za a iya tusa keyarsu zuwa gida Afghanistan.
Gwamnatin Burtaniyar dai ta ce tsugunnar da mutanen abu ne da ke gabanta har a yanzu.
