News
Shugaba Recep Tayyip Erdogan ya sha rantsuwar kama aiki
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Shugaba Recep Tayyip Erdogan ya sha alwashin karfafa dangantakar diflomasiyya da sauran kasashen duniya a yayin da ya dauki alkawarin inganta tattalin arzikin Turkiyya.
Zababben shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya sha alwashin karfafa dangantakar diflomasiyya da sauran kasashen duniya a yayin da ya dauki alkwarin kara inganta tattalin arzikin kasar, tare da samar da sabbin sauye-sauyen da za su ciyar da kasar gaba.
Firaministan kasar Indiya ya ci alwashin hukunta masu sakaci a haɗarin jiragen ƙasa
Erdoghan ya fadi hakan ne bayan shan rantsuwar shugabancin kasar a sabon wa’adin mulki a karo na uku a wannan Asabar a sakamakon nasarar da ya samu a zagaye na biyu na zaben kasar da ya gudana a makon da ya gabata. Shugabannin kasashen duniya akalla 21, da firaminista 13 ne ke halartar bikin shan rantsuwar na Erdogan a birnin Ankara.
