News
Yan sanda sun kuɓutar da yara tara a Zamfara
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya ta kubutar da wasu kannana yara tara da ‘yan bindiga suka sace.
A cikin wata sanarwa da Rundunar ‘yan sandan jihar ta fitar mai ɗauke da sa hannun kakakin rundunar jihar ASP Yazid Abubakar, ya ce a ranar 3 ga watan Yuni ne rundunar ta samu bayanai daga dagacin ƙauyen Gora Namaye cewa ‘yan bindiga sun sace wasu yara maza da mata waɗanda suka tafi neman itace a jeji.
Dan Takarar Gwamna A Kogi Ya Dauki Malamin Firamare A Matsayin Mataimaki
Sanarwar ta ce bayan samun labarin ne ‘yan sanda tare da hadin gwiwwa jami’an tsaro suka ƙaddamar da bincike domin ceto yaran, lamarin da ya sa suka samu nasarar ceto yaran tara, tare da mayar da su hannun iyayensu.
Rundunar ta ce tana ci gaba da gudanar da bincike domin kamo maharan tare da gurfanar da su a gaban kotu.
A ranar Asabar ne ‘yan bindigar suka kai hari tare da sace yaran a ƙauyen Gora da ke cikin yankin ƙaramar hukumar Maradun a jihar zamfara.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
