News
Rikicin Shugabanci Ya Kunno Kai A Majalissar Dokokin Jihar Nasarawa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
An samu bayyanar wakilai biyu dake ikirarin samun kujerar jagorantar majalisar dokoki ta 7 a jihar Nasarawa.
Ibrahim Balarabe da Daniel Ogazi dukkansu daga shiyyar yammacin jihar sune wakilan biyu dake ikirarin shugabancin kuma dukkansu ‘yan APC ne.
INEC Ta Amince Da Sunayen ‘Yan Takarar Gwamna A Jahohin Bayelsa, Kogi Da Imo.
A jiya Talata 6 ga watan Yuni ne aka shirya kaddamar da majaliisar ta 7 da kuma zaben kakakin majalisar da mataimakinsa amma magatakardan majalissar ya sanar da dage zaben saboda dalilan tsaro.
Daga karshe mambobi 11 ne suka zabi Ibrahim Balarabe da Jacob Kudu a matsayin kakakin majalisa da mataimakinsa a daya daga cikin ma’aikatun jihar inda mukaddashin magatakardar majalisar Ibrahim Musa ya rantsar da su.
Amma an zabi Ogazi da Adamu Oyanki a matsayin kakakin majalisa da mataimakinsa da wakilai 13 a harabar majalisar.
Bayan haka Gwamna Abdullahi Sule ya karbi bakuncin Balarabe da Kudu da sauran ‘yan tsaginsa a fadar gwamnatin jihar Nasarawa da ke birnin Lafiya.
