News
Ana gudanar da babban zabe a Saliyo
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ana gudanar da zabe a kasar Saliyo inda sama da mutum miliyan uku da ke kasar ta Yammacin Afirka ke layi domin zabar shugabanninsu, ciki har da shugaban kasa.
An samu mutane sun fito daidai gwargwado a sassan kasar da suka hada da gundumomin Old Town da Bo da Kono da Karene da Pujehun.
Bashin Da Ake Bin Najeriya Yanzu Ya Doshi Tiriliyan 50 – DMO
Zuwa yanzu, rahotanni daga rumfunan zabe sun nuna cewa zaben na tafiya lami lafiya. Akwai jinkiri wurin bude kayayyakin zabe a wasu daga cikin rumfunan zabe da ke Kondebotihun a Old Town da Dwarzark da New England Ville duka da ke Freetown babban birnin kasar.
A rumfunan zabe da dama, an soma jefa kuri’a da misalin bakwai na safe a ranar Asabar. Ana rade-radin cewa zaben shugaban kasar da kuma na ‘yan majalisa zai yi zafi matuka tsakanin ‘yan takara, a daidai lokacin da ake kiraye-kirayen zaman lafiya da kuma rikicin tsadar rayuwa da ake fuskanta tun daga 2022.
Kasar Saliyo wadda ba ta farfado ba ta fannin tattalin arziki tun daga 1991 zuwa 2022 bayan yakin basasa da Annobar Ebola bayan shekara goma, da kuma annobar korona sun kara tasiri a kanta da kuma yakin Ukraine.
