News
Bom Ya Kashe Mutum 100 A Somaliya
DAGA ABDULKADEER TUKUNTAWA
Shugaban Kasar Somalia, Hassan Sheikh Mohamud ya tabbatar da cewa akalla mutum 100 ne aka kashe sakamakon wasu hare-haren kunar bakin wake biyu da aka kai da motoci a wajen Ma’aikatar Ilimi ta kasar.
An kai harin ne a ranar Asabar a Mogadishu, babban birnin kasar, inda akalla mutum 300 suka samu raunuka daban-daban.
Bidiyon Sabbin Naira 2000 Da 5000 Na Karya Ne —Bincike
Mista Mahmud ya kai ziyara wurin da aka kai harin inda waɗanda suka shaida lamarin suka bayyana cewa cikin mintoci kaɗan motocin suka kaddamar da hare-haren.
Shaidu sun bayyana cewa ita motar ta biyun ma ta kai harin ne a yayin da jama’a suka garzayo da kuma motar daukar marasa lafiya domin kai agaji.
Babu wata kunigiya da ta dauki nauyin kai harin zuwa yanzu amma kungiyar al-Shabab da ke da alaka da Al-Qaeda ta sha kaddamar da irin wadannan hare-hare.
Kungiyar ta al-Shabab ta yi sanadin mutuwar dubban mutane a kasar ta Somalia da kuma raba miliyoyi da muhallansu.
A ’yan kwanakin nan gwamnatin kasar ta rika zafafa hare-hare kan ’yan kungiyar, lamarin da ya jawo ita ma kungiyar ke zafafa hare-hare.
Ko a kwanakin baya sai da kungiyar ta kai hari a wani otel inda ta kashe mutane da dama.
