News
Yan daba sun kashe wani Dan kasuwa har lahira a Kano
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wasu ’yan daba a ranar Talata a kauyen Dakasoye da ke karamar Hukumar Garun Malam ta Jihar Kano, sun kashe wani dan kasuwa mai suna Alhaji Auwalu Gambo, da sanyin safiyar ranar Litinin.
Lamarin ya jefa kauyen cikin tsoro da bacin rai yayin da ‘yan bindigar suka je gidan wanda abin ya shafa suka daba masa wuka har ya mutu.
Da take magana a gidan rediyon Freedom, matar marigayin, Yahanaso Gambo, ta ce sun zo ne da misalin karfe 3 na safe a lokacin da suke barci suka wuce dakinsa kai tsaye.
Ta ce ko da yake ba su yi magana da ita ba, sun daure mijinta da igiya suka fara dukansa wanda hakan ya janyo zubar da jini sosai.
Ta ce, “Sun tsallaka ta katangar makwabtanmu. Su kusan biyar ne. Muna barci sai suka ce mu farka. Sai suka fara daba wa mijina wuka suka karya masa sassa da dama na jikinsa. Ba su tsaya ba har sai da ya mutu.”
Ita ma mahaifiyar marigayin, Hajiya Hamu Kabiru wadda ita ma tana zaune a gida daya ta ce, “Bayan sun kashe shi ne suka ce in ba su kudi; wanda na yi. Sun yi barazanar kashe ni idan ban koma dakina ba. Muna kallo ne suka kashe shi.”
A halin da ake ciki, mazauna yankin sun koka kan hare-haren da ‘yan daba ke kaiwa, inda suka yi kira ga gwamnatin jihar da ta kawo musu dauki.
Wani mazaunin garin Aminu Muhammad Ilyas ya ce “Muna fuskantar babban kalubale a wannan yanki. Mutane suna zuwa akai-akai don ko dai su yi fashi ko kuma su kashe mutane. Muna son gwamnati ta taimaka mana ta magance wannan matsalar.”
Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce ana ci gaba da bincike kan lamarin.
