News
An ceto mutum 30 daga hannun ƴan bindiga a Kebbi
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
An ceto mutane akalla 30 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a yankin Danko Wasagu da ke jihar Kebbi.
Waɗanda aka ceto ɗin sun fito ne daga garin Kontagora na jihar Neja da Danmari da Kaba da kuma Kajiji a jihar Zamfara da kuma Bena ta jihar Kebbi.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa shugaban karamar hukumar Danko Wasagu, Alhaji Useni Aliyu Bena ne ya bayyanawa manema labarai game da rahoton ceto mutanen.
Ya kuma yaba wa gwamnatin jihar kan yadda take aiki da jami’an tsaro, tare da ba su tallafi domin ganin an fatattaki ‘yan fashin dajin da suka addabi jihar da ma maƙwabtanta, tare da kuɓutar da waɗanda aka yi garkuwa da su.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News1 day ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News2 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
