News
Dole Gwamnatoci Su Kare Masu Fallasa Rashawa A Afirka – Amnesty
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kungiyar kare hakkin bil’adam ta Amnesty International, ta ce dole ne kasashe yammaci da tsakiyar Afirka su daina cin zarafin masu bankaɗo ayyukan rashawa, a maimakon hakan sai a dauki matakan kare su.
Jiya ne aka cika shekara 20 da cimma yarjejeniya kasashen Afirka ta kiyayewa da kuma yaki da rashawa.
NNPCL ya kama jirgin ruwa dauke da danyen mai na sata da za a kai Kamaru
Babbar sakatariya a kungiyar ta Amnesty, Agnes Callamard, ta ce “Irin halin da masu fallasa rashawa ke shiga a kasashen yammaci da tsakiyar Afirka abin babu dadi, wadannan mutanen fa mutane ne da ke taka muhimmiyar rawa da sadaukarwa wajen yaki da cin hanci da rashawa, to amma sai kaga daga karshe su ake kai wa hari ko wulakanta su saboda kawai sun bayyana gaskiya.”
Ta ci gaba da cewa,” Dole ne gwamnatoci su tashi tsaye wajen kare hakkin dan’adam da girmama masu kwarmata irin waɗannan bayanai da ma biya musu dukkan bukatunsu saboda rawar da suke takawa wajen bayyana marassa gaskiya.”
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
