Connect with us

News

Za a kafci naira bilyan 70 a yi wa sabbin ‘Yan Majalisar Tarayya watanda, manoman ƙasar nan kuma tallafin bilyan 19

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

Gwamnatin Bola Tinubu za ta raba wa sabbin ‘yan Majalisar Tarayya naira biliyan 70, manoma a ba su tallafin naira biliyan 19.

Amma kuma manoma waɗanda suka yi gagarumar ambaliya a 2020, a faɗin ƙasar nan, za a raba masu Naira bilyan 19.

Advertisement

Matakan Tinubu 12 Na Wadata Ƙasa Da Abinci

Wannan bayani na ƙunshe cikin wani ƙudirin da Majalisa ta amince da shi a ranar Alhamis.

PREMIUM TIMES ta bada labarin cewa yadda ‘yan Majalisar Tarayya su ka ce albashin su ba ya isar su, har sun fara cin bashi.

Advertisement

Mambobin Majalisar Tarayya sun tayar da ƙurar neman a yi masu albashi mai tsoka, saboda tsadar rayuwa da ake fama.

Ba albashi kaɗai su ka yi magana ba, har ma da alawus-alawus.

Advertisement

Fito da wannan magana ya haifar da ruɗani a zaman Laraba, har Shugaban Majalisar Tarayya Tajuddeen Abbas ya ce a shiga taron musamman.

Daga nan kuma sun ce har yanzu fa ba a biya su albashi da alawus ba, har sun fara cin bashi.

Advertisement

Wanda ya halasci taro, amma ya ce a sakaya sunan sa, ya ce albashi da alawus ɗin ba ya isar su tafiyar da ayyukan su da sauran harkokin su.

Amma kuma ya ce ba a yi maganar albashin su na watan jiya ba.

Advertisement

Shugaban Majalisar Tarayya Tajuddeen Abbas, ya ce maganar albashi mai tsoka, magana ce babba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending