News
KAROTA ta sami nasarar cafke wasu matasa biyar masu sojojan gona da hukumar
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta jiha KAROTA ta sami nasarar cafke wasu matasa biyar masu sojojan gona da hukumar
Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka a yau ta cikin wata sanarwa da Kakakin Hukumar ta KAROTA Nabilusi Abubakar Kofar Nai’sa ya sanya wa hannu
Dalilan Da Ya Sa Shugaban Jamiyyar APC Na Kasa Ya Yi Murabus
Ya bayyana cewa an jima ana kawo ƙorafi hukumar cewa jami’anta na matsawa al’umma da karɓe-karɓen kuɗi
Bayan zurfafa bincike a wannan rana an sami nasarar cafke mutum biyar daga cikin wadanda ake zargin
Sanarwar ta bayyana cewa Shugaban Hukumar ya ce za a dauki matakin gurfanar da su a gaban Yansanda domin zurfafa bincike tare da ɗaukar matakin da ya dace.
Shugaban ya roƙi al’umma da su ci gaba da bawa Hukumar KAROTA haɗin kan da ya dace domin gudanar da ayyukanta bisa tsarin doka da oda.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
